Shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje, ya mayar da martani mai zafi ga Buba Galadima bisa kalaman da ya yi na cewa Ganduje ya rasa tasirin siyasa.
A wata sanarwa da mai taimaka masa kan wayar da kan jama’a, Cif Oliver Okpala, ya fitar, Ganduje ya bayyana Galadima a matsayin “ɗan siyasa da ya mutu, aka yi watsi da shi, kuma yana cikin fargaba” wanda ba shi da wani tasiri a siyasar Najeriya.
Okpala ya ce Galadima ba shi da kwarjini, kuma yana da tarihin sauya ra’ayi akai-akai don amfanin kansa.
Ya tunatar da jama’a cewa Galadima ya kasance cikin tawagar Buhari a baya amma ya kasa taimaka mata wajen cin zaɓe a lokacin.
Ya yaba wa nasarorin Ganduje a lokacin da yake gwamnan Jihar Kano, yana mai cewa ayyukansa har yanzu suna bayyana kuma yana da farin jini a tsakanin al’umma-Albarka Radio FM